Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya wato CAN reshen jihohi 19 na arewacin Najeriya ta taya Shugaba Muhammadu Buhari murnar nasara cin zaben shugaban kasa da aka gudanar makon da ya gabata.
An dai zabi Buhari a zaben kasar da aka gudanar ranar 23 ga watan Faburairu inda ya kayar da babban abokin adawar sa na jam’iyar PDP, Atiku Abubakar wanda tuni ya yi watsi da sakamakon zaben.
A wata wasika da kungiyar ta aikewa shugaban kasa mai dauke da kwanan watan 1 ga watan Faburairu, kungiyar ta CAN reshen arewacin Najeriya,ta ce nasarar da Buhari ya samu wata sheda ce dake nuna gaskiyarsa.
Ƙungiyar ta kuma yi kira ga shugaban kasar da ya kafa gwamnatin da za ta hada mutane daga kabilu daban-daban dake kasarnan.